About this episode
Shirin na wanan makon zai soma ne daga Tarayya Nigeria inda kisan Fatima Abubakar ƴar shekara 35 a duniya da ƴaƴanta 6 da wasu marasa imani su kayi ranar 17 ga wanan watan a Unguwar Ɗorayi Chiranchi da ke Kano ya girgiza duniya . Wanan kisan da ke zaman mafi muni da aka gani a yan taakanin nan ya sake fito da girman matsalar dabanci da ke addabar wanan jihar mafi yawan al’umma a arewcin Najeriya. Zargin sace Christoci sama da 100 yayin da suke tsaka da ibada ranar 18 ga wanan watan a karamar Kajuru na Jihar Kaduna a arewacin Najeriya ya tayar kura matuka a makon da mu kayi bankwana kamar yadda Joseph Bawa guda daga cikin yan uwan mutanen da akayi garkuwa dasu ya tabbatar wa RFI. Waɗannan da ma wasu na ƙunshe a cikin shirin na Mu Zagaya Duniya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.