About this episode
A ranar Larabar da ta gabata shugaban Amurka Donald Trump ya nanata barazanar ɗaukar matakin soji na ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin ‘yan ta’adda a Najeriya, inda kuma ya ƙara caccakar gwamnatin ƙasar kan gaza ɗaukar matakin hana kisan kiyashin da ya ce ana yi wa Kiristoci a ƙasar.