About this episode
Ɗaruruwan ‘yan Najeriya a jiya Litinin, sun gudanar da zanga-zangar lumana a birnin Abuja, domin bayyana ɓacin ransu dangane da jan ƙafa a kan gyaran dokar zaɓe da majalisar ƙasar ke yi, musamman kan matakinta na ƙin amincewa da batun tilasta wa hukumar zaɓe sakin sakamako kai-tsaye daga rumfuna a shafinta na yanar gizo.Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Barista Ibrahim Bello Rigachikun, tsohon ɗan Majalisar Tarayya, kuma ƙwararren lauya a Najeriyar. Latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar